Zhao Lijian: Taron sassa 4 wani yunkuri ne na dakile kasar Sin
2022-02-11 20:24:40 CRI
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Zhao Lijian, ya ce taron da manyan jami’an kasashen Amurka da Japan, da Australia da India suka shirya gudanarwa, wani salo ne na yunkurin dakile kasar Sin.
Zhao wanda ya bayyana hakan a Juma’ar nan, yayin taron manema labarai da ya gudana, ya ce sassan 4 na da burin amfani da taron na su, domin tattauna abun da suka kira “Karuwar tasirin Sin”.
Jami’in ya kara da cewa, wannan salo ne da Amurka ke bi domin wanzar da danniya, kuma hakan zai harzuka wasu sassa, tare da haifar da fito na fito, tare da gurgunta hadin gwiwar sassan kasa da kasa.
Zhao Lijian ya yi kira ga kasashen duniya, da su yi watsi da tsohon tsarin cacar baka, su gyara kura kuran su, game da kafa tawagogin da za su rika yiwa saura kallon hadarin kaji, ko raba kan kasashen duniya. Kaza lika ya bukaci sassan kasa da kasa, da su ba da gudummawa, wajen wanzar da zaman lafiya da daidaito a yankin Asiya da tekun fasifik.
A Juma’ar nan ne, sakataren wajen Amurka Antony Blinken, ya gana da ministocin harkokin wajen kasashen Japan, da Australia, da India a birnin Melbourne. (Saminu)
Labarai Masu Nasaba
- Zhao Lijian: Sin na fatan sassan kasa da kasa za su yi hadin gwiwa wajen taimakawa tsibiran dake tekun Fasifik
- Sin ta bukaci Amurka da ta kawar da karin haraji da takunkumai da ta kakaba mata
- Sin da Amurka za su gudanar da jerin ayyuka na tunawa da ziyarar da tsohon shugaban Amurka Richard Nixon ya gudanar a Sin
- Likitancin Gargajiyar Kasar Sin Ya Taimaka Wa Gu Ailing Eileen Ta Samu Lambar Zinariya