Sin da Amurka za su gudanar da jerin ayyuka na tunawa da ziyarar da tsohon shugaban Amurka Richard Nixon ya gudanar a Sin
2022-02-10 19:59:23 CRI
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Zhao Lijian, ya ce Sin da Amurka za su gudanar da wasu jerin ayyuka, na bikin cika shekaru 50 da ziyarar da tsohon shugaban Amurka Richard Nixon ya gudanar a Sin, inda ya kuma sanya hannu kan sanarwar Shanghai.
Zhao wanda ya bayyana hakan a yau Alhamis, ya ce sanarwar Shanghai, ita ce irin ta ta farko da kasashen biyu suka sanya hannu, wadda ta kafa wasu ka’idoji da sassan biyu za su bi, domin bunkasa kawancen su, musamman tabbatar da manufar “kasar Sin daya tak a duniya”, wadda ta zama ginshikin daidaita alakar sassan biyu, da kuma kafa huldar diflomasiyya tsakanin su. (Saminu)
Labarai Masu Nasaba
- Rundunar sojojin kasar Sin ta sha alwashin dakile duk wani yunkuri na tsoma hannun sassan waje cikin harkokin cikin gidan kasar
- Sin: Ya dace duk wata cudanya ta kasa da kasa ta dace da zamani
- Zhao Lijian: Bai dace a yi amfani da mizani biyu a yaki da ta’addanci ba
- Sin ta bukaci Amurka da ta kawar da yiwuwar sayarwa Taiwan da makamai