Sakatare Janar na MDD ya aike da sakon taya murna ga wasannin Olympics na Beijing
2022-02-04 21:00:52 CMG
Yayin da ake bude wasannin Olympics na lokacin hunturu na 2022 na Beijing da yammacin yau Asabar, Sakatare Janar na MDD Antonio Guterres ya aike da sakon taya murna ta kafar bidiyo, inda ya bayyana ruhin wasannin a matsayin na zaman lafiya da fahimta da girmama juna. (Fa’iza Mustapha)