Sin: Shugaban kasar Argentina zai halarci bikin bude gasar Olympics ta lokacin sanyi ta Beijing, da kuma ziyartar kasar Sin
2022-01-26 21:18:18 CRI
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Zhao Lijian, ya bayyana a yayin taron manema labaru na yau da kullum Larabar nan cewa, shugaban kasar Argentina Alberto Fernández zai halarci bikin bude gasar wasannin Olympics na lokacin sanyi na Beijing, zai kuma ziyarci kasar Sin daga ranar 4 zuwa 6 ga watan Fabrairu. Wannan ita ce ziyarar farko da shugaba Alberto Fernández zai kai kasar Sin.