Shugabannin Sin da Isra’ila sun taya juna murnar cika shekaru 30 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin kasashensu
2022-01-24 11:51:38 CRI
A yau Litinin, Shugaban kasar Sin Xi Jinping, shi da takwaransa na Isra’ila, Isaac Herzog, suka yi musayar sakonnin murnar cika shekaru 30 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin kasashensu.
Shi ma firaministan kasar Sin Li Keqiang ya yi musayar sakon taya murnar da takwaransa na Isra’ila, Naftali Bennett, a yau Litinin. (Fa’iza Mustapha)