logo

HAUSA

Koriya ta arewa ta harba makami mai linzami tekun gabashin Koriya ta kudu

2022-01-17 14:50:55 CRI

Koriya ta arewa ta harba makami mai linzami tekun gabashin Koriya ta kudu_fororder_220117-Ahmad-Koriya ta arewa

Babban jami’in tawagar dakarun tsaron hadin gwiwa na Koriya ta kudu JCS, ya bayyana a yau Litinin cewa, Koriya ta arewa DPRK ta harba makami mai linzami da ba a tantance nau’insa ba zuwa tekun gabashin Koriya ta kudu, koda yake ba a yi cikakken bayani kan lamarin ba.

Wannan shi ne karo na hudu da DPRK ta harba makamai masu linzami a wannan shekarar.

Kamfanin dillancin labaran DPRK ya bayyana a makon jiya cewa, Koriya ta arewan ta yi nasarar gwaje-gwajen makamai masu linzamin biyu a ranar Juma’a.

Koriya ta arewan ta ce ta yi nasarar gwajin makamai masu linzami masu matsanancin gudu a ranar 5 da kuma 11 ga watan Janairu. (Ahmad)