‘Yan fashin daji sun kashe a kalla mutane 58 a hare-hare a arewa maso yammacin Najeriya
2022-01-09 16:14:16 CRI
A kalla mutane 58 ‘yan fashin daji suka kashe a hare-haren da suka kai wasu kauyuka a kananan hukumomi biyu na jahar Zamfara dake shiyyar arewa maso yammacin Najeriya.
Ibrahim Bello Zauma, kakakin gwamnan jahar Zamfara Bello Matawalle, ya shedawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua a yayin zantawa ta wayar tarho cewa, hare-haren sun faru ne a ranakun Laraba da Alhamis a kauyuka da dama dake kananan hukumomin Anka da Bukkuyum dake jahar.
Zauma ya kara da cewa, kawo yanzu, an samu hasarar rayukan mutane 36 a karamar hukumar Bukkuyum, da kuma mutuwar wasu 22 a karamar hukumar Anka.
Ya ci gaba da cewa, gwamnan jahar ya ziyarci yankunan da lamarin ya faru domin yin ta’aziyya ga mutanen yankunan sakamakon hare-haren da ‘yan fashin dajin suka kaddamar a yankunan.
A cewar kafafen yada labaran wurin, kimanin kauyuka hudu aka cinnawa wuta a hare-haren wanda aka fara a ranar Laraba. Kuma jami’an tsaron sa kai na bijilanti wadanda suka yi kokarin dakile hare-haren na daga cikin wadanda aka kashe a hare-haren.
Zauma ya nuna cewa, gwamnatin jahar tana ci gaba da aiwatar da dabarun kawo karshen hare-haren ‘yan bindigar a jahar.(Ahmad)
Labarai Masu Nasaba
- Yawan mutanen da suka kamu da nau’in Omicron a Najeriya ya kai 51
- Najeriya ta janye dakatarwar da ta yiwa kamfanin jiragen saman Emirates
- Masanin Najeriya: Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Wadatar Da Kowa A Kasar Ya Cancanci Kasashe Masu Tasowa Su Koya
- Adadin wadanda ‘yan bindiga suka hallaka a Kaduna sun kai mutum 38