Sabon magajin garin New York: ya kamata fadar White House ta nemi gafarar Amurkawa ’yan asalin Asiya
2022-01-07 16:15:32 CRI
Kamfanin dillancin labarai na Bloomberg ya bada rahoto a ranar 4 ga wata yayin wata tattaunawa, inda sabon magajin garin birnin New York Eric Adams ya bukaci fadar White House da ta fito bainar jama’a ta nemi afuwar Amurkawa ’yan asalin Asiya game da kalaman batanci da tsohon shugaban kasar Amurka Donald Trump ya yi inda yake kiran "cutar kasar Sin" yayin da aka samu barkewar sabuwar annobar. (Ahmad Fagam)