Guturres ya nuna alhinin mutuwar tsohon shugaban kasar Sin
2022-12-01 14:22:01 CMG Hausa
Babban sakataren MDD Antonio Guterres, ya bayyana cewa, ya kadu matuka da samun labarin mutuwar tsohon shugaban kasar Sin Jiang Zemin.
A madadin MDD, yana mika sakon ta’aziyya ga iyalan Jiang da gwamnatin kasar Sin da ma daukacin al’ummar Sinawa. (Ibrahim)