Xi zai tattauna da Biden kan huldar Sin da Amurka da sauran batutuwan dake shafarsu
2022-03-18 09:57:47 CMG Hausa
Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Hua Chunying, ta sanar a jiya Alhamis cewa, da yammacin yau Jumma’a 18 ga watan Maris, shugaban kasar Sin Xi Jinping zai tattauna da shugaban kasar Amurka Joe Biden, bisa goron gayyatar da ya gabatar masa, inda za su tattauna game da dangantakar Sin da Amurka da sauran batutuwan dake shafarsu. (Ahmad)