An wallafa jawabin da Xi ya yi a taron ministocin FOCAC karo na 8
2021-12-28 19:14:39 CRI
An wallafa muhimmin jawabin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar a wajen bude taron ministoci karo na takwas na dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC).
Xi ya gabatar da jawabinsa mai taken "A kiyaye al'adar tsayawa tsayin daka tare da gina al'ummar Sin da Afirka mai kyakkyawar makoma a sabon zamani" a ranar 29 ga watan Nuwamba.(Ibrahim)