An bukaci al’ummar Somaliya su goyi bayan kokarin tabbatar da zaman lafiyar kasar yayin da ake fama da kalubaloli
2021-12-16 10:16:00 CRI
Kwamandan Burundi mai barin gado na tawagar dakarun wanzar da zaman lafiya na kungiyar tarayyar Afrika a Somaliya (AMISOM), ya bukaci ‘yan kasar Somaliya da su goyi bayan kokarin tawagar don tabbatar da zaman lafiyar kasar yayin da ake fama da kalubaloli masu yawa.
Telesphore Barandereka, kwamandan Burundi mai barin gado na tawagar dakarun(AMISOM, ya bayyana cikin wata sanarwar da aka fitar a Mogadishu, babban birnin kasar Somaliya cewa, wannan muhimmiyar dama ce da ya samu a matsayinsa na jami’in sojin Afrika wajen bayar da gudummawarsa don wanzar da zaman lafiya a kasar Somaliya, da shiyyar, da nahiyar Afrika, har ma ga zaman lafiyar duniya baki daya, sakamakon yadda ayyukan ta’addanci suka kara karade duk duniya. Jami’in ya bukaci ‘yan kasar Somaliya su goyi bayan kokarin da gwamnatin kasar ke yi da abokan hulda na kasa da kasa suke yi domin a samu nasarar maido da zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar.(Ahmad)
Labarai Masu Nasaba
- Wang Yi ya tattauna da ministan harkokin wajen Somalia Ahmed IsseAwad
- AU ta ce annobar COVID-19 ta baiwa duniya damar gina sabon tsarin kiwon lafiya don tinkarar matsalolin lafiya a nan gaba
- Mahalarta taron demokaradiyya: Kasashen Afrika na da ‘yancin zabar salon shugabancinsu
- Tsokaci Kan Huldar Kasuwanci Da Tattalin Arziki Tsakanin Sin Da Afrika