Sin ta bayyana matukar adawar ta ga takunkumin da Amurka ta kakabawa wasu kamfanonin kasar 12
2021-11-25 20:32:46 CRI
Kakakin ma’aikatar cinikayyar kasar Sin Shu Jueting, ta ce gwamnatin Sin ta bayyana matukar adawar ta ga takunkumin da Amurka ta kakabawa wasu kamfanonin ta 12, kuma tuni Sin din ta mika koken hakan ga tsagin Amurka.
Shu Jueting ta bayyana hakan ne yayin taron manema labarai na yau Alhamis, lokacin da aka gabatar mata da tambaya kan hakan. Ta ce Amurka tana fakewa da sunan tsaro wajen kakaba takunkumi maras tushe ga kamfanonin Sin. (Saminu)