logo

HAUSA

ECOWAS za ta nemo matakai masu dorewa na warware rikicin siyasar Guinea

2021-09-17 09:57:15 CRI

ECOWAS za ta nemo matakai masu dorewa na warware rikicin siyasar Guinea_fororder_210917-ahmad-1-Ecowas

Shugabannin kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika  (ECOWAS), sun fara gudanar da muhimmin taron koli a ranar Alhamis game da batun juyin mulkin sojoji a kasar Guinea.

Taron kolin shi ne karo na biyu da shugabannin kasashen 15 na shiyyar kudancin hamadar Afirka suka gudanar tun bayan yujin mulkin sojoji a ranar 5 ga watan Satumba.

Shugaban kungiyar ECOWAS, Nana Addo Dankwa Akufo-Addo, ya bayyana kwarin gwiwa cewa kungiyar za ta lalibo matakai masu dorewa na warware rikicin siyasar kasar Guinea. A yayin jawabin bude taron,  Akufo-Addo ya ce, wadannan matakai suna da matukar muhimmanci wajen tabbatar da dorewar zaman lafiyar siyasa da kwanciyar hankali da kuma hadin kan shiyyar. (Ahmad)