Mali ta dage takunkuman da ta kakabawa tsohon shugaban riko na kasar da Firaministansa
2021-08-28 17:09:46 CRI
Kwamitin kula da mika mulki a kasar Mali, ya yi maraba da matakin gwamnatin riko na kasar, na dage takunkuman da ta kakabawa tsohon shugaban rikon kwarya, Bah N’Daw da Firaministansa Moctar Ouane.
Wata sanarwa da kwamitin ya fitar jiya, ta kuma yi maraba da matakan da gwamnatin ta dauka na tabbatar da sun amfana daga hakkokin da suke da shi a matsayinsu na tsohon shugaban kasa da tsohon Firaminista. (Fa’iza Mustapha)