logo

HAUSA

Manoman Xinjiang sun samu karin kudin shiga daga noman Almonds

2021-04-17 16:12:12 CRI

Manoman Xinjiang sun samu karin kudin shiga daga noman Almonds_fororder_1

Gundumar Shache, ta jihar Xinjiang ta kasar Sin, sansani ne na noman Almonds mafi girma a kasar Sin, wadda akewa lakabi da “garin Almonds”, inda ake noman Almonds din a gonaki masu fadin hekta sama da dubu 66. A cikin ‘yan shekarun da suka gabata, manoman gundumar sun samu karin kudin shiga daga noman Almonds.

Manoman Xinjiang sun samu karin kudin shiga daga noman Almonds_fororder_2

Misali, manomi Tohti Turdi ya je kamfanin Ameti da aka kafa a gundumar, dauke da gyadar Almonds da ya ajiye a cikin jakuna da dama domin sayar da su, inda manajan kamfanin, Muhtarjan Mulaniyaz ya saye duka.

Manoman Xinjiang sun samu karin kudin shiga daga noman Almonds_fororder_3

Yanzu kamfanin Ameti yana sayar da Almonds zuwa ga birnin Tianjin da lardin Henan da lardin Anhui da sauran lardunan kasar. A ko wace shekara, adadin kudin da kamfanin yake samu daga sayar da Almonds ya kai kudin Sin yuan biliyan daya, a sa’i daya kuma, kamfanin yana samar da guraben aikin yi ga matasan iyalan dake fama da talauci, har ya kai su ga fita daga kangin talauci.(Jamila)