logo

HAUSA

Tattaunawa da Harouna Sani, wanda ke malanta a kasar Sin<?xml:namespace prefix = o ns = "urn:schemas-microsoft-com:office:office" />

2020-03-07 20:49:39 cri



Daga karshen watan Faburairu zuwa farkon watan Maris na kowace shekara, dalibai a nan kasar Sin kan kammala hutun lokacin sanyi,sai kuma su koma makaranta, su fara zangon karatunsu na biyu. Sai dai a bana, ma'aikatar ilmi ta kasar Sin ta fitar da sanarwar da ta bukaci a jinkirta komawar dalibai makaranta, domin dakile yaduwar cutar numfashi ta Covid-19. Duk da haka, malaman makaranta ba su daina ayyukan koyarwa ba, kuma dalibai ma ba su daina karatu ba.

Wakilinmu Ibrahim Yaya, ya tattauna da Harouna Sani, wanda yake koyar da harshen Hausa a jami'ar koyon harsunan waje ta lardin Heibei na kasar Sin, domin jin yadda aikin koyarwa da karatu ke gudana a wannan lokaci na musamman. Ga kuma yadda hirar tasu ta kasance.