Hira da Samaila Usman dan Najeriya dake karatu a jami'ar Lanzhou ta kasar Sin
2020-03-01 17:10:23 cri
A yayin da ake himmatuwa wajen dakile yaduwar annboar cutar numfashi ta COVID-19 a kasar Sin, sashin Hausa na CRI ya ci gaba da zantawa da wasu daliban Najeriya wadanda ke karatu a sassa daban-daban na kasar, domin jin ra'ayoyinsu kan matakan da gwamnatin kasar Sin ke dauka na ganin bayan cutar.
A yau ne, wakilinmu Murtala Zhang ya zanta da da Samaila Usman, wani dalibi dan jihar Yobe wanda ke karatun digiri na uku a jami'ar Lanzhou dake arewa maso yammacin kasar Sin.
Samaila Usman ya bayyana ra'ayinsa game da managartan matakan da hukumar makarantarsu ke dauka domin kare dalibai daga kamuwa da cutar numfashi ta COVID-19, inda a cewarsa, ma'aikatan jinyar kasar sun cancanci yabo saboda babbar gudummawar da suka bayar wajen shawo kan wannan cuta.