Augusto ya bayyana hakan ne a Luanda, bayan wata ganawa tsakanin tawagar wakilan kasashen biyu.
Ya jaddada bukatar dake akwai na sake farfado da kyakkyawar hadin gwiwar hukumomin kasashen biyu, a matsayin hadin gwiwar da za ta farfado da dukkan yarjejeniyoyin da aka cimma, da kuma yarjejeniyoyin fahimtar juna da aka rattaba hannu kansu tsakanin kasashen biyu.
A nasa bangaren, ministan harkokin wajen Cape Verde Luis Filipe Tavares, ya jaddada matsayin kasarsa na yin hadin gwiwa da Angola a fannoni da suka hada da harkokin soja da tsaro. (Ahmad Fagam)