in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Iran ta kwashi kashinta a hannun Spaniya a wasan 'yan kasa da shekarau 17
2017-10-25 21:25:29 cri
Kafafen yada labarai na cikin gida sun rawaito cewa, kasar Andalus ta lallasa Iran da ci 3-1 a wasan cin kofin duniya na FIFA na 'yan kasa da shekaru 17 a wasan daf da kusa dana karshe wanda aka buga a Kochi, na kasar India.

Cikin mintoci 13 kachal da fara wasan, Abel Ruiz ya budewa Spaniya da zara kwallon farko.

Dan wasan kungiyar mai amfani da kafar hagu Sergio Gomez, ya samu nasarar zara kwallo ta biyu a wani bugu da yayi daga waje mai nisa.

Mintoci 7 bayan kwallon ta biyu, Ferran Torres ya kara kwallo ta uku.

Saeid Karim shine ya zarawa Iran kwallo mintoci 69 da fara wasan, sai dai hakan bai wadatar ba.

Iran ta samu nasarori har guda hudu da suka hada da Guinea da ci (3-1), sai Jamus da ci (4-0), da Costa Rica da ci (3-0) da kuma Mexico da ci (2-1).(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China