Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2008-06-05 21:29:12    
Taron koli na mata na duniya ya nuna goyon baya ga kasar Sin wajen yaki da bala'in girgizar kasa

cri

A gun taron koli na ministoci mata na duniya, da aka shirya a ran 5 ga wata a birnin Hanoi, a madadin taron koli ne, shugabar kwamitin da ke kula da harkokin taron kolin na wannan karon, Madam Irene Natividad ta nuna tausayi da jejeto ga mata da yara na kasar Sin da suke shan wahalar girgizar kasa.

Madam Natividad ta ce, taron koli ya yanke shawarar ba da taimakon kudi na karo na farko da yawansu ya kai kudin Amurka dala dubu 5 ga yankunan da ke fama da girgizar kasa, domin taimakawa mata da yara na wadannan yankuna. Ban da wannan kuma, taron koli ya kaddamar da wani asusu domin ci gaba da neman kudin kyauta da aka bayar. A sa'i daya kuma, Madam Natividad ta yi kira ga dukkan mahalartan taron da su bayar da kudin kyauta cikin yakini.

Shugabar tawagar wakilai ta kasar Sin, kuma mataimakiyar ministan kasuwanci ta kasar Sin Madam Ma Xiuhong ta nuna godiya cikin sahihiyar zuciya ga goyon baya da kuma kudin kyauta da taron koli ya bai wa kasar Sin.(Danladi)