Ran 2 ga wata da yamma, yara 89 da malamai 16 daga wuraren da ke fama da bala'in girgizar kasa na lardin Sichuan sun sauka birnin Sanya na lardin Hainan domin karbar aikin jiyya kan hankali ta hanyar yawon shakatawa wanda za a shafe kwanaki 15 ana yinsa.
Lardin Hainan yana da kyawawan wurare, yara da suka jikata a sakamakon al'amarin Beslan na kasar Rasha sun taba karbar jiyya a wannan wuri. Hukumomin da abin ya shafa na lardin Hainan sun shirya wannan aiki domin kwanta da hankulan yara da suka taba shan wahalar bala'in girgizar kasa na lardin Sichuan.
Yayin da suke yin yawon shakatawa a lardin Hainan, yara za su kai ziyara ga wurare dabam daban na lardin Hainan, kuma wasu kwararu za su ba da taimako kan hankulansu. An ce, lardin Hainan yana da kyawawan sharudda wajen kwantar da hankulan yara.
|