Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2008-05-20 22:06:33    
Jama'ar kasar Sin suna nuna alhini ga mutanen da suka mutu sabo da girgizar kasa ta hanyoyi daban-daban

cri
Daga ran 19 ga wata, Jama'ar da ke wurare daban-daban na kasar Sin suna bin hanyoyi daban-daban domin nuna alhini ga mutanen da suka mutu sabo da girgizar kasa da ta faru a gundumar Wenchuan ta lardin Sichuan, kuma suna yin addu'a don yin fatan alheri ga jama'ar da fama da bala'in.

A ran 19 ga wata a birnin Jincheng na lardin Shanxi, da binin Hangzhou na lardin Zhejing, mutanen birane sun yi nadin furanni da takarda, kuma sun sa furannin cikin ruwa, a birnin Shenzhen kuma, mutane sun daura kyallaye masu launin rawaya a hannayensu, sun yi haka ne duk domin yin addu'a ga mutanen da suka mutu, da yin fatan alheri ga mutanen da suke da rai.

A ran 19 ga wata da yamma da misalin karfe 2 da minti 28, shugabannin kasar Sin ciki har da Hu Jintao da Jiang Zeming da Wu Bangguo da Wen Jiabao dukkansu sun yi tsit tare da jama'a 'yan kabilu daban-daban na duk kasar domin nuna alhini ga mutanen da suka mutu sakamakon girgizar kasa.

Ya zuwa karfe 6 na ran 20 ga wata da yamma, girgizar kasa da ta faru a lardin Sichuan ta yi sanadiyar mutuwar mutane 40,075, yayin da wasu mutane dubu 240 suka jikkata. Majalisar gudanarwa ta kasar Sin ta tsai da cewa, kwanaki 3 wato daga ran 19 zuwa 21 ga wata za su zama ranakun zaman makoki.(Umaru)