Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2008-05-20 21:48:45    
Wajibi ne a dauki hakikanan matakai don magance bala'un da aka samu a sakamakon girgizar kasa, a cewar mataimakin firayin ministan kasar Sin

cri
A likacin da Mr. Hui Liangyu, mataimakin firayin ministan kasar Sin ke yin bincike kan halin bala'in girgizar kasa da lardin Sichuan ke ciki, ya nuna cewa, tilas ne a mayar da kwanciyar hankali ta jama'a a matsayin farko, kuma wajibi ne a dauki hakikanan matakai, don magance bala'un da aka samu a sakamakon girgizar kasa, ta yadda za a hana kara samun mutuwar mutane.

Bayan faruwar girgizar kasa a gundumar Wenchuan ta lardin Sichuan, an samu hadari a matarin ruwa da yawa, kuma a wasu wurare an samu bala'un zaizayewar duwatsu, da na kwararowar kasa, kazalika kuma an lalata wasu na'urorin fitar da adanan kayayyaki masu guba, da kuma bututun man fetur da na gas.

Mr. Hui Liangyu ya ce, a lokacin da ake magance bala'un da aka samu a sanadiyar girgizar kasa, a waje daya kuma, ya kamata a dauki hakikanan matakai, don tabbatar da kwanciyar hankali ta wadanda ke ayyukan ceto, da na likitanci, da kuma na sa kai. (Bilkisu)