Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2008-05-16 17:13:01    
Kungiyoyin duniya sun yaba wa ayyukan ceto da gwamnatin Sin take yi

cri
Bayan da aka yi mummunar girgizar kasa mai karfin digiri 7.8 na ma'aunin Richter a gundumar Wenchuan ta lardin Sichuan na kasar Sin a ran 12 ga wata, a kwanan baya, kasashen duniya sun nuna goyon baya ga kokarin da gwamnatin Sin da jama'ar Sin suke yi wajen fama da girgizar kasar da kuma gudanar ayyukan ceto. Wasu shugabannin kungiyoyin duniya da na yankuna sun nuna yabo ga kasar Sin bisa kyawawan ayyukan ceto da take yi cikin sauri.

A lokacin da yake zantawa da wakilin gidan rediyo na Majalisar Dinkin Duniya, Stephen Martin, wani kwararren hukumar kiwon lafiya ta duniya wato WHO, wanda yake kula da shirin shawo kan cututtuka da harkokin ba zata na jin kai ya bayyana cewa, gwamnatin Sin tana gudanar da ayyukan ceto cikin sauri yadda ya kamata. Abubuwan da take yi na da matukar muhimmanci wajen rage yiwuwar barkewar cututtuka masu yaduwa.

Sa'an nan kuma, ran 15 ga wata da dare, Jean Ping, shugaban kwamitin kungiyar tarayyar Afirka wato AU ya ba da sanarwar cewa, kwamitin AU ya nuna yabo da goyon baya ga gwamnatin Sin da jama'ar Sin bisa kokarin da suke yi domin fama da girgizar kasa da kuma ayyukan ceto da suke yi a yanzu. Yana fatan wadanda suka jikkata a girgizar kasar za su samu sauki cikin sauri.(Tasallah)