An sami girgizar kasa mai tsanani a gundumar Wenchuan ta lardin Sichuan na kasar Sin a ran 12 ga wata, wadda ya yi sanadiyar mutuwar mutane da yawa, haka kuma, an yi hasarar dimbin dukuyoyi.
Ran 13 ga wata, shugaba Umar Musa Yar adua na kasar Nijeriya ya aiko da talgiram zuwa ga shugaba Hu Jintao na kasar Sin, inda ya nuna bakin cikinsa sosai saboda girgizar kasar ta yi sanadiyar mutuwar mutane masu tarin yawa da yin hasarar dimbin dukiyoyi, ya nuna wa gwamnatin Sin da jama'ar Sin juyayi da goyon baya cikin sahihanci. (Tasallah)
|