Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2008-04-04 17:07:01    
Jihar Tibet za ta tallafa wa 'yan kasuwa wadanda suka samu hasara a cikin matsalar 3·14

cri
Hukumar kula da harkokin jama'a ta jihar Tibet mai cin gashin kanta ta kasar Sin ta bayar da labari cewa, tun daga watan Maris da ya gabata, hukumomin gwamnatin jihar Tibet za su tallafawa otel-otel da dakunan abinci da kamfanonin kasuwanci da sauran 'yan kasuwa masu zaman kansu wadanda suka samu hasara a cikin matsalar nuna karfin tuwo mai tsanani da aka yi a ran 14 ga watan Maris domin tabbatar da zaman rayuwarsu na yau da kullum.

Mr. Xu Jianzhong, mataimakin direktan hukumar kula da harkokin jama'ar jihar Tibet ya bayyana cewa, za a tallafawa 'yan kasuwa a fannonin tallafin zaman rayuwar yau da kullum da na jiyya, wato za a samar da wasu kudade ga 'yan kasuwa wadanda ba su iya tabbatar da zaman rayuwarsu ba, kuma za a samar da taimako ga wadanda suke neman aikin jiyya a asibiti. (Sanusi Chen)