Ran 3 ga wata da yamma, jami'an jakadancin kasashen waje da ke kasar Sin wadanda suka halarci bikin bude zama na farko na majalisar bada shawara kan harkokin siyasa a karo na 11 sun ce, suna jaran taron wasannin Olympic na Beijing mai zuwa na shekarar 2008.
Mr. Mabure jakadancin kasar Tanzania da ke kasar Sin ya ce, yana zura ido kan taron wasannin Olympic na Beijing da za a bude a watan Agusta na shekarar da muke ciki, kuma ya yi imanin cewa, wajibi ne kasar Sin za ta ci nasarar yi wannan muhimmin taron wasanni.
Ban da haka kuma, jami'an jakadancin kasashen waje sun yabawa manyan nasarorin da kasar Sin ta samu a cikin shekaru 30 da suka wuce tun ta fara yin gyare-gyare a gida da bude kofa ga kasashen waje, Mr. Mabure ya ce, jama'ar kasar Sin sun shiga zamani mai kudi daga halin fama da talauci, wannan nasara mafi girma da kasar Sin ta samu.
|