A ran 1 ga wata a birnin Beijing, kakakin hukumar sa ido kan abinci da magunguna ta kasar Sin Madam Yan Jiangying ta bayyana cewa, hukumomin kasar Sin da abin ya shafa suna kokarin dauki matakai, don tabbatar da aikin samar da magunguna don yaki da bala'i.
Game da bala'in dusar kankara da aka yi a kwanakin nan a kundancin kasar Sin, madam Yan Jiangying ya bayyana cewa, hukumar sa ido kan abinci da magunguna na kasar ta riga ta dauki matakai cikin gaggawa, tana mai da hankali kan aikin samar da magugunna da kayayyakin likita, don tabbatar da aikin ajiye da samar da magunguna da ke warkar da cutar mura da ta ciwon sanyi da ta ciwon ciki. Ban da wannan kuma, za ta kara karfin sa ido kan abinci da magunguna, masamman na rigakafin matsalar ingangcin abinci da ke shafa da mutane da yawa a wadansu wurare dake da taron mutane kamar tasoshin jiragen kasa da hanyoyi da dai sauransu. (Zubairu)
|