Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2007-04-19 18:52:41    
Kasar Sin tana fata bangarori daban daban da ke da nasaba da batun Darfur za su dauki matakai masu yawa bisa manyan tsare-tsare

cri
Yau 19 ga wata, kakakin ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin Liu Jianchao ya bayyana a nan birnin Beijing cewa, kan batun shiyyar Darfur ta kasar Sudan, ya kamata bangarori daban daban da abin ya shafa su dauki matakai masu yawa bisa manyan tsare-tsare, amma ba tattauna kan sanya takunkumi ba. Kasar Sin tana fata za a tabbatar da ra'ayi daya da bangarori daban daban suka samu tun da wuri.

A gun taron manema labaru da aka shirya a wannan rana, Mr. Liu Jianchao ya ce, kwanan baya, gwamnatin kasar Sudan ta amince da shiri na mataki na biyu a duk fannoni dangane da girke sojojin hadin kan M.D.D. da kungiyar tarayyar kasashen Afrika, wato kungiyar AU a shiyyar Darfur, wannan shi ne wani ci gaba mai kyau da aka samu. A wannan lokacin da aka samu ci gaba kan batun Darfur, ya kamata banagrori daban daban su dauki matakai masu yawa bisa manyan tsare-tsare, domin sa kaimi ga tabbatar da ra'ayi daya da abin ya shafa da aka samu. (Bilkisu)