Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2007-04-11 18:22:13    
Firayin ministan kasar Sin ya fara yin ziyara a kasar Japan

cri

Bisa gayyatar da takwaransa na kasar Japan Abe Shinzo ya yi masa ne, Mr. Wen Jiabao, firayin ministan kasar Sin ya isa birnin Tokyo domin fara yin ziyarar aiki a kasar Japan. Wannan ne karo na farko da firayin ministan kasar Sin ya kai wa kasar Japan ziyara bayan shekaru 7 da suka wuce.

A cikin jawaninsa da ya bayar a filin jirgin sama na Tokyo, Mr. Wen ya bayyana cewa, shekarar da muke ciki shekara ce ta cikon shekaru 35 da kafuwar dangantakar diplomasiyya a tsakanin kasar Sin da kasar Japan. Yanzu yunkurin kyautata da raya dangantakar da ke tsakaninsu yana da muhimmiyar dama. Makasudin wannan ziyararsa shi ne kara amincewa da juna a fannin siyasa da karfafa hadin guiwa irin ta moriyar juna da habaka yin musanye-musanye na sada zumunta domin ciyar da dangantakar da ke tsakanin kasashen Sin da Japan gaba cikin hali mai dorewa a cikin dogon lokaci mai zuwa. Yana fatan za a kai dangantakar makwabtaka irin ta sada zumunta da ke tsakanin Sin da Japan har wani sabon mataki ta wannan ziyarar da yake yi a Japan. (Sanusi Chen)