A ran 10 ga wata, a birnin Seoul, babban birnin kasar Korea ta Kudu, Wen Jiabao, firayim ministan kasar Sin da ke yin ziyarar aiki a kasar ya gana da takwaransa na kasar Han Duck-Soo.
Firayim ministocin biyu sun darajanta sakamako mai kyau da aka samu a cikin wadannan shekaru 15 da kasashen Sin da Korea ta Kudu suka kulla huldar diplomassiya tsakaninsu, kuma sun yi musanyar ra'ayoyinsu kan yadda za a ci gaba da sa kaimi ga bunkasuwar dangantakar abokantaka ta hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu daga dukkan fannoni.
Bayan ganawar, sun gana da wakilan matasa na kasashen Sin da Kora ta Kudu tare.(Kande Gao)
|