Ran 8 ga wata, an gabatar da shirin doka kan ikon mallakar dukiyoyi ga babban taron majalisar wakilan jama'ar kasar Sin wato hukumar koli ta kasar don yin bincikenta. Dokar kuma tana jawo hakulan jama'a sosai. Malam Wang Zhaoguo, mataimakin shugaban zaunannen kwamitin majalisar ya yi bayani a kan dokar a gun taron. Bisa shirin dokar, kasar Sin za ta kiyaye ikon mallakar dukiyoyin jama'a da na mutane masu zaman kansu cikin daidaici.
Dokar wata doka ce mai muhimmanci sosai ga tsarin dokoki na kasar Sin. Bisa shirin dokar, ba ma kawai kasar Sin za ta kiyaye halalen kudin shiga da gidaje da abubuwan zaman rayuwa na mutane masu zaman kansu ba, har ma za ta kiyae kudin ajiye da kudin jari da kudin ruwa da suka samu.
A cikin shekarun nan biyar da suka wuce, zaunanen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin ta taba yin bincike a kan wannan shirin dokar har sau 7. (Halilu)
|