|
 |
 |
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye | more>> |
|
 |
|
 |
|
|
 |
(GMT+08:00)
2007-03-06 18:55:25
|
 |
Kasar Sin tana ganin cewa, ya kamata a dauki mataki wajen yin ma'amala ga juna cikin daidaici a tsakanin kasa da kasa
cri
 Yau ranar 6 ga wata, Mr. Li Zhaoxing, ministan harkokin waje na kasar Sin ya bayyana cewa, kaidojin aiki na M.D.D. sun kayyade cewa, ana zaman daidaici a tsakanin duk kasashen duniya, bangaren Sin yana ganin cewa, yin ma'amala cikin daidaici ba wata maganar diplomasiya ba ce, kamata ya yi a dauki mataki wajen wannan. Yanzu, bangaren Sin yana kokari domin tabbatar da wannan.
A gun taron manema labaru na taron shekara-shekara na majalisar wakilan jama'ar Sin, Mr. Li Zhaoxiang ya ce, tilas ne kasar Sin ta mai da aikin kara hadin gwiwa tare da sauran kasashe masu tasowa a matsayin tushen ayyukan harkokin waje nata. Shugaba Hu Jintao na kasar Sin ya taba yi bayani kafin ya kai ziyara a kasashe 8 na Afrika cewa, ya kamata mu fahimci wahalhalun da abokanmu na Afrika suke fuskantar a yanzu, kuma mu yi shawrawarin zumunci tare da su, da kuma yin hakikanin hadin kai na samun moriyar juna, musamman ma a fannonin warware matsalar zaman rayuwar jama'a, da kara karfin samun bunkasuwa da kansu. (Bilkisu)
|
|
|