Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2007-02-09 17:27:49    
Shugaba Hu Jintao ya bar birnin Maputo na kasar Mozambique, bayan da ya kawo karshen ziyarar aiki a kasar

cri

Hu Jintao da Eduardo Joaquim Mulembwe

Shugaba Hu Jintao na kasar Sin ya bar birnin Maputo, babban birnin kasar Mozambique a ran 9 ga wata, bayan da ya kawo karshen ziyarar aiki a kasar, kuma ya nufi kasar Seychelles, domin ci gaba da ziyararsa a kasashe 8 na Afrika.

A filin jirgin sama, Mr. Armando Emilio Guebuza, shugaban kasar Mozambique ya shirya gagarumin bikin ban kwana ga shugaba Hu Jintao da kuma 'yan rakiyarsa.

A wannan rana kuma, shugaba Hu Jintao ya halarci bikin bude cibiyar gwaji ta fasahohin sha'anin noma da kasar Sin ta ba da taimako ga Mozambique.

A lokacin ziyararsa a Mozambique, shugaba Hu Jintao ya yi shawarwari da shugaba Guebuza, kuma ya gana da Mr. Eduardo Joaquim Mulembwe, shugaban majalisar dokoki na Mozambique. Bayan haka kuma, kasashen Sin da Mozambique sun bayar da hadaddiyar sanarwa. (Bilkisu)