Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-11-05 21:21:28    
Hadin gwiwar da ke tsakanin Sin da Afirka yana amfana wa bangarorin 2

cri
Ran 5 ga wata, a nan Beijing, ministan harkokin waje na kasar Sin Li Zhaoxing ya bayyana cewa, hadin gwiwar da ke tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka yana amfana wa bangarorin 2.

A gun taron manema labaru da ya yi tare da takwarorinsa na kasashen Habasa da Masar a ran nan, Mr. Li ya bayyana cewa, anihin hadin gwiwar da ke tsakanin Sin da Afirka a fannonin tattalin arziki da ciniki da kuma sha'anin zaman al'ummar kasa shi ne yin zaman daidai wa daida da moriyar juna da kuma taimakon juna. Ya kara da cewa, kasar Sin da kasashen Afirka suna fuskantar damar bunkasuwa mai kyau, a sa'i daya kuma, suna fuskantar kalubale iri daban daban da kuma iri daya. Bangarorin Sin da Afirka za su daidaita su yadda ya kamata a sakamakon yin hadin gwiwa a tsakaninsu.(Tasallah)