Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-11-04 17:19:30    
Sin za ta ba da babban taimako wajen bunkasa tattalin arzikin Afrika, in ji mataimakin shugaban Bankin Duniya

cri
Ran 3 ga wata, a nan birnin Beijing, Malam Gobind Nankani, mataimakin shugaban Bankin Duniya mai kula da harkokin nahiyar Afrika ya bayyana cewa, kasar Sin tana kara ba da babban taimakonta ga kasashen Afrika don bunkasa harkokin tattalin arzikinsu ta hanyar cinikiya da zuba jari.

Yayin da Nankani ke karbar ziyara da manema labaru suka yi masa, ya bayyana cewa, an sami babban ci gaba wajen inganta hadin guiwar tattalin arziki da ciniki a tsakanin Sin da kasashen Afrika cikin shekarun nan da suka wuce, yawan kudin jari da kasar Sin ta zuba a nahiyar Afrika ya dauki kashi 10 cikin dari bisa jimlar kudin jarin nan. Yanzu, kasashen Afrika suna cin gajiyar kudin jari da kasar Sin ke kara zubawa. Ya gabatar da shawara ga kasashen Afrika da su dauki matakai masu yakini don kara rage yawan kudi da suke kashewa wajen yin cinikayya, da kyautata manyan ayyukansu da guraben zuba jari, ta yadda za su kara jawo kudin jari daga kasar Sin. (Halilu)