A ran 1 ga wata, a cikin wata wasikar da ya mika wa jaridar Financial Times ta kasar Birtaniya, Paul Wolfowitz, shugaban bankin duniya ya bayyana cewa, bunkasuwar kasar Sin ta samar da sakamako mai kyau ga Afirka.
A cikin wasikar, Mr. Wolfowitz ya ce, a cikin shekaru 25 da suka gabata, Sinawa fiye da miliyan 300 sun fitar da kansu daga kangin talauci. Sinawa sun nemi wata hanyar samun bunkasuwa bisa basirarsu, sabo da haka kasar Sin ta samar da sakamako mai kyau ga 'yan Afirka miliyan 600 da ke kudancin hadamar Sahara wadanda suke yin kokari domin neman samun hanyar fitar da kansu daga talauci.
Ban da wannan kuma Mr. Wolfowitz ya bayyana cewa, bankin duniya yana so inganta hadin gwiwa tsakaninsa da kasar Sin domin sa kaimi ga bunkasuwar Afirka, kuma bangarorin biyu za su karfafa yin tattaunawa tsakaninsu kan batun.(Kande Gao)
|