Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-11-02 11:17:59    
Shugaban kasar Burundi yana fatan kamfanonin kasar Sin masu yawa za su zuba jari a kasarsa

cri
A ran 1 ga wata, yayin da shugaban kasar Burundi Pierre Nkurunziza ke yin ziyara a birnin Shenzhen na kasar Sin, ya bayyana cewa, kasar Budundi za ta aiwatar da manufar bude kofarta ga kasashen waje, kuma tana fatan kamfanonin kasar Sin masu yawa za su je kasar don zuba jari.

Lokacin da yake ganawa da Liu Yingli, mataimakin magajin birnin Shenzhen, shugaba Nkurunziza ya bayyana cewa, kasar Burundi ta fitar da kanta daga yake-yake na shekaru 10 ba da jimawa ba, yanzu tana farfado harkokin raya tattalin arziki da sha'anin kasuwanci, da kuma aiwatar da manufar bude kofarta ga kasashen waje. Kasar Burundi tana fatan za ta iya koyon fasahohi masu zamani na kasar Sin, haka kuma tana fatan kamfanonin kasar Sin masu yawa za su je kasar domin zuba jari da samun bunkasuwa.(Kande Gao)