Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-10-30 11:28:58    
Birnin Beijing zai bai wa muhimman baki na Afirka hidima bisa halin musamman na ko wane bako

cri

Tun daga ran 3 zuwa ran 5 ga watan Nuwamba, za a shirya taron koli da taron ministoci na dandalin tattaunawar hadin guiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka a nan birnin Beijing. Lokacin da ake yin taron, birnin Beijing zai bai wa baki na Afirka hidimomi bisa halin musamman na kowane bako.

Shugabannin kasashen Afirka za su sauka a otel-otel masu matsayin taurari 5 guda 22 a birnin Beijing lokacin da suke halartar taron. Wadannan otel-otel suna share fagen maraba da zuwan shugabannin kasashen Afirka, kuma suna shirya hidimomi bisa halin musamman na kowanensu. Ma'aikata wadanda za su yi hidima ga shgabannin a cikin otel-otel, za su iya gaishe da wadannan shugabanni da harsunan Turanci da Faransanci har da yaren kasashensu. Sa'an nan kuma, an buga sunayen shugabanni da na matansu a kan riguna da silifofi da za su sanya lokacin da suke kwana a cikin dakin shugaba na otel-otel.

Bugu da kari kuma, wadannan otel-otel sun riga sun kebe dakunan dafa abinci ga kuku-kuku na shugabannin kasashen Afirka, kuma za su samar da abinci da abin sha iri iri ga kungiyoyin wakilan kasashen Afirka bisa bukatar da suke nema. (Sanusi Chen)