Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-09-23 21:36:46    
Kamaru tana fatan kasar Sin za ta kara ba ta taimako a fannin fasaha

cri
Yayin da shugaban kwalejin nazarin huldar da ke tsakanin kasa da kasa ta kasar Kamaru ke hira da manema labaru na kasar Sin a kwanan baya, ya ce, 'ina fatan kasar Sin za ta kara baiwa Kamaru taimako a fannin fasahohi, kuma ina fatan za a tsara hakikanin shiri na ba da taimakon.'

Ya ce, tun bayan da aka kulla huldar diplomasiyya a tsakanin Kamaru da Sin, huldar da ke tsakanin kasashen biyu ta yi ta bunkasa lami lafiya, kuma an yi ta inganta hadin gwiwar da ke tsakaninsu, kasar Sin ta bayar da babban taimako da tallafin fasaha ga kamaru a fannin bunkasuwar tattalin arzikinta. Game da taron dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka da za a yi a watan Nuwamba mai zuwa a nan birnin Beijing, ya jaddada cewa, kara tabbatar da ayyukan hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka a hakika, zai zama babban makasudin Kamaru a wajen halartar taron nan. Ban da wannan, ya kuma yi fatan taron zai zama wani dandalin da za a inganta hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka da kuma Sin da Kamaru daga dukan fannoni.(Lubabatu)