Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-08-31 20:29:22    
Kasar Portugal za ta aika da sojoji 140 da za su shiga sojojin MDD da ke kasar Lebanon

cri

Ran 30 ga wata, kwamitin koli na tsaro na kasar Portugal ya tsai da kudurin cewa, za ta aika da sojoji 140 zuwa kasar Lebanon don shiga sojojin wucin gadi na MDD da ke kasar.

Janar Demelo kakakin kwamitin koli na tsaro na kasar Portugal ne ya ba da wannan labari cewa, Anibal Cavaco Silva shugaban kasar Portugal da Jose Socrates firaministan kasar sun halarci taron da kwamitin ya yi a wannan rana. Bisa bukatar da MDD da kungiyar gammayar kasashen Turai suka yi, an tsai da kudurin aika wa da runduna mai sojoji 140 zuwa kasar Lebanon don shiga ayyukan kiyaye zaman lafiya da MDD ke tafiyarwa.