Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-08-21 10:37:42    
Kasashen Larabawa sun yi alkawarin ba da taimako ga kasar Lebanon don farfado da kasar bayan rikicin Lebanon da Isra'ila

cri

Wakilin Rediyon kasar Sin ya ruwaito mana labari cewa , a ran 20 ga watan nan a birnin Alkahira , hedkwatar kasar Masar , ministocin harkokin waje da wakilan kasashen Larabawa sun yi taro , inda suka yi alkawarin ba da taimako ga kasar Lebanon don farfado da kasar .

A wannan rana ministocin da wakilan kasashe mambobi 22 na Kungiyar tarayyar kasashen Larabawa sun halarci taron kan matsalar Lebanon . Mahalartan taron sun yi na'am da kai gundumuwa ga kasar Lebanon wadda kasar Isra'ila ta kaiwa farmaki sau da yawa a yankin . Za a sanar da hakikanin shirin kai agaji a taron ministocin kudi na kasashen Larabawa a watan Satumba .

Mahalartan sun kuma bayar da sanarwa , inda suka la'anci kasar Isra'ila saboda ta taka kuduri mai lambar 1701 na Kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya zartas a ran 19 ga watan Agusta . (Ado)