A ran 19 ga wannan wata, babban kwamandan rundunar soja na kasar Iran Mohammad Hassan dadras ya bayyana cewa, sojojin kasa na kasar Iran za su kara karfinsu na tsaron kasa bisa hakikanin halin da suke ciki tare da sakamako.
Bisa labarin da Kamfanin da ake kira " Fars News Agency" ya bayar, an ce, a lokacin da Mr Dadras ya jagoranci rawar daji da sojoji suke yi a wannan rana, ya bayyana cewa, idan aukuwar takadamar a wurin da suke ciki , to sojojin kasa na kasar Iran za su kara karfinsu na tsaron kasa bisa matsayin kalubalen da aka yi musu ta yadda za su iya hana kowane aikin kai hari da aka yi ga kasar Iran tare da sakamako. Ya bayyana cewa, a cikin gajeren lokaci, sojojin kasa na kasar Iran sun sami makamai da yawa da ke da fasahar zamani sosai, a cikin sojojin kasa na kasar , rundunar sojojin harba makamai masu linzami suna da babban karfin hakika, a matakin nan gaba, za su yi gwajin harba makamai masu linzami da za a iya sarrafa su.(Halima)
|