Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-08-16 11:11:39    
Kasar Iran ba za ta amince ba da kudurin kwamitin sulhu kan batun nukiliya na kasar Iran, in ji shugabanta

cri

Ran 15 ga wata, a birnin Ardebil da ke arewa maso yammacin kasar Iran, shugaban kasar Iran Mr. Mahmoud Ahmadinejad ya bayyana cewa, kasar Iran ba za ta amince da kuduri mai lamba 1696 da kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya zartas da shi a kan batun nukiliya na kasar Iran a kwanan baya ba.

A gun wani taron jama'a da aka yi a ran nan, Mr. Ahmadinejad ya yi bayanin cewa, kada kwamitin sulhu ya tilasta wa kasar Iran ta amince da wannan kuduri, wajibi ne ya gane cewa, kasar Iran ba za ta yi rangwame saboda barazanar da aka yi mata ba.

Ban da wannan kuma, Mr. Ahmadinejad ya ce, a kwanan baya, ya amsa wayar tarho daga babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya Mr. Kofi Annan, inda ya bukaci kasar Iran da ta amsa shirin kasashe 6 da kasashen duniya suka bayar. Ya gaya wa Mr. Annan cewa, kasar Iran tana son warware matsala ta hanyar yin tattaunawa, amma kudurin da kwamitin sulhu ya zartas da shi ya sa kasar Iran ta canza shawara.(Tasallah)