Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-08-11 18:07:39    
Isra'ila ta ci gaba da jefa boma bomai a arewacin kasar Lebanon, kasar Rasha ta gabatar da shirin kuduri dangane da rikicin da ake yi a tsakanin Lebanon da Isra'ila

cri

A ran 11 ga wata da alfijir, jiragen sama na sojojin Isra'ila sun ci gaba da jefa boma bomai a arewacin kasar Lebanon da kudancin birnin birnin Beirut, babban birnin kasar Lebanon. Wannan ya riga yi yi sanadiyyar mutuwar mutane a kalla 11 a yayin da mutane 9 suka ji rauni.

Bisa labarin da muka samu, an ce, a ran 10 ga wata da dare, kasar Rasha ta riga ta bayar da wani shirin kuduri ga mambobin kwamitin sulhu 15 na MDD, inda ta yi kira ga bangarorin Lebanon da Isra'ila da su tsagaita bude wuta cikin awoyi 72 nan da nan, domin kungiyoyin ba da agaji na duniya su ba da taimakon jin kai.

Bisa labarin da kafofin watsa labaru na kasar Isra'ila suka bayar, an ce, zaunannen wakilin kasar Isra'ila a MDD Dan Gillerman ya riga ya ki yarda da wannan shirin kuduri da kasar Rasha ta gabatar.(Danladi)