Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-07-19 11:53:36    
Kasar Iran tana fatan samun ci gaba wajen shawarwarin nukiliya da ake yi a tsakaninta da kungiyar tarrayar kasashen Turai

cri
Ran 18 ga wata, Mahmud Ahmadinejad, shugaban kasar Iran ya ce, kasarsa tana fatan samun ci gaba kan matsalar nukiliya ta kasar Iran ta hanyar yin shawarwari da kungiyar tarrayar Turai.

A wannan rana a gun babban taron wakilan daliban kasar Iran, Mr. Ahmadinejad ya yi jawabi cewa, yin amfani da fasahar makamashin nukiliya wani iko ne na kasar Iran da ba a iya kwacewa ba, amma a sa'i daya kuma, kasar Iran tana fatan samun ci gaba kan matsalar nukiliya ta kasar Iran ta hanyar yin shawarwari da kungiyar tarrayar Turai, da kuma yin amfani da fasahar makamashin nukiliya cikin lumana a cikin filin da hukumar makamashin nukiliya ta duniya ta kayadde. Ya jadadda cewa, bai kamata kasar Amurka ta kawo matsaloli a cikin gudanarwar ba, sabo da za ta sanya a samu da bambancin ra'o'yi a tsakanin bangarori daban daban da ke cikin shawarwarin. Haka kuma, za a kawo tasiri ga bangarorin da ke da nasaba da matsalar nukiliya ta Iran. (Bilkisu)