Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-06-30 10:42:52    
Kungiyar kasashe 8 tana bukatar warware matsalar nukiliya ta kasar Iran ta hanyar siyasa

cri
Ran 29 ga wata a gun taron ministocin harkokin waje na kungiyar kasashe 8 da aka shirya a birnin Moscow, an bayar da wata sanarwa cewa, kungiyar kasashe 8 tana ta tsayan kan warware matsalar nukiliya ta kasar Iran ta hanyar siyasa. Sanarwar tana ganin cewa, daddale wata yarjejeniya mai dorewa a dukan fannoni, ba kawai zai sanya jama'ar kasar Iran su yi amfani da makamashin nukiliya ba, har ma zai kawo moriya mai dorewa wajen siyasa da tattalin arziki ga kasar Iran.

Sanarwar ta ce,kungiyar kasashe 8 sun nuna amincewa ga shawarwarin da Ali Larijani, sakataren kwamitin tsaron kasar Iran, da Javier Solana, babban wakilin tarayyar kasashen Turai mai kula da harkokin waje da manufar kwanciyar hankali za su yi a ran 5 ga watan Yuli, tana fata kasar Iran za ta ba da hakikanin amsa. (Bilkisu)