Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-06-20 11:10:32    
Shugaban Kasar Iran ya jaddada cewa ba zai karbi shawarwarin nukiliya tare da 'karin sharadi ba

cri
Wakilin Rediyon kasar Sin ya ruwaito mana labari cewa , a ran 19 ga watan nan a birnin Tehran , Mahmoud Ahmadi Nejad , Shugaban Kasar Iran ya jaddada cewa , ba zai karbi shawarwarin nukiliya tare da 'karin sharadi ba . A wannan rana shugaba Bush na kasar Amurka ya sake neman kasar Iran da ta daina aikace-aikacen ingancin uranium.

Gidan talabijin na kasar Iran ya watsa labari cewa , Mr. Nejad ya yi wannan bayani ne yayin da yake ganawa da Ayatollah Khamenei , shugaban koli na kasar Iran . Sa'an nan kuma ya nuna yabo ga sabon shirin da kasashe 6 suka gabatar don warware matsalar nukiliyar Iran . Ya ce , wannan mataki mai yakini ne da kasashen duniya suka gabatar . (Ado)