Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-06-19 17:02:27    
Ziyarar firaminista Wen Jiabao a Afirka za ta bude sabuwar kofar zuba jari da kungiyoyin jama'a na Sin da Afirka ke yi

cri
Ziyarar da firaministan kasar Sin Mr. Wen Jiabao ke yi a kasashe 7 na Afirka ta jawo hankulan kungiyoyin tattalin arziki na jama'a da rukunin masana'antu na kasashen Sin da Afirka sosai, suna ganin cewa, ziyarar Mr. Wen za ta bude sabuwar kofar zuba jari da kugniyoyin jama'a na kasashen Sin da Afirka suke yi.

Lokacin yake zantawa da manema labaru a ran 19 ga wata, shugaban sashen yin cudanya na hadadiyyar kungiyar kasuwanci ta jama'a ta kasashen Sin da Afirka Mr. Chu Shuntang ya bayyana cewa, kungiyar wakilai ta kasar Sin da ke karkashin jagorancin Mr. Wen a wannan gami tana kunshe da wakilan rukunin masana'antu masu zaman kansu na kasar Sin, haka kuma, a cikin kasashe 7 na Afirka da Mr. Wen zai kai musu ziyara akwai masana'antu masu zaman kansu na kasar Sin masu yawa, tabbas ne ziyarar da za a yi a wannan gami za ta ingiza yin mu'amalar tattalin arziki a tsakanin kungiyoyin jama'a na kasashen Sin da Afirka, ta yadda kungiyoyin jama'a na kasar Sin za su kara zuba jari a kasashen Afirka.(Tasallah)